Sunday 8 February 2026 - 22:16
Haɗin kan ƙasa da Biyayya ga Jagora su ne Garkuwar Iran daga Maƙiya

Hauza/ Hujjatul Islam wal Muslimin Farrokhfal ya jaddada cewa ƙarfin tsarin Musulunci yana dogara ne ga "Wilayatul Faqih", kuma maƙiya ba zasu iya fuskantar goyon bayan al'umma ga jagorancin juyin juya hali ba.

A cewar rahoton Ofishin Yada Labaran Hauza, Hujjatul Islam wal Muslimin Ahmad Farrokhfal, a wajen taron sanya wa ɗaliban addini rawani a birnin Khoy, yayin taya murnar ranakun zagayowar nasarar juyin juya hali, ya bayyana cewa tsarin Jamhuriyar Musulunci ci gaban tafarkin jagorancin Allah ne. Ya ce: "Jajircewar al'ummar Iran na tsawon shekaru arba'in da bakwai a gaban kawancen Gabas da Yamma, yana nuna ƙarfin nufin da aka gina a ƙarƙashin inuwar Wilayatul Faqih."

Wilayatul Faqih; Katangar ƙarfen tsarin Musulunci

Mamban ƙungiyar malamai na makarantun Hauza ta Qom, yayin yin ishara ga muhimmiyar rawar da jagoran juyin juya hali yake takawa wajen fuskantar makirce-makirce, ya bayyana cewa: "Jagora cikin basira ya kare ƙasar daga kowace irin fitina. Maƙiya su sani cewa 'Wilaya' ita ce katangar ƙarfe na wannan hema, kuma duk wani katsalandan gare shi ba zai tafi a banza ba."

Rashin nasarar dabarun tsoratarwa na maƙiya

Shugaban sakatariyar majalisar ƙoli ta Hauza ya bayyana matsin lambar maƙiya a matsayin yunƙurin banza na tsoratar da mutane. Ya ce: "Tarihi ya nuna cewa duk lokacin da al'ummar Iran suka haɗa kai a cikin gida, su kan tilasta maƙiya su ja da baya. A yau ma, hanyar fuskantar matsin lamba ita ce kiyaye haɗin kan ƙasa."

Makarantun Hauza; Masu tallafawa al'umma

Hujjatul Islam wal Muslimin Farrokhfal ya kuma yi nuni da nauyin da ya rataya a wuyan malamai, inda ya tunatar da cewa: "Makarantun Hauza koyaushe su ne masu jagorancin harkar addini da zamantakewa. Kasancewar malamai a lokacin matsaloli kamar Korona da girgizar ƙasa, shaida ce ta dangantaka mai ƙarfi tsakanin malamai da mutane."

A ƙarshe, ya yi kira ga sabbin ɗalibai da su san muhimmancin nauyin da ke kansu na yada koyarwar Ahlul Baiti (A.S), yana mai jaddada cewa: "Malami na gaskiya shi ne wanda, kamar yadda kur'ani ya koyar, ba ya tsoron kowa sai Allah, kuma yake tafiya cikin jajircewa don isar da saƙon Allah da kiyaye alaƙar al'umma da Wilaya."

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha